Jihar Adamawa za ta yi rigakafin yara sama da miliyan 1.3 daga 2 zuwa 5 ga Mayu

0
Jihar Adamawa za ta yi rigakafin yara sama da miliyan 1.3 daga 2 zuwa 5 ga Mayu

Jihar Adamawa za ta yi rigakafin yara sama da miliyan 1.3 daga 2 zuwa 5 ga Mayu

Spread the love

Gwamnatin Jihar Adamawa tare da haɗin gwiwar UNICEF da sauran abokan hulɗa sun bayyana ƙudurin su na kare lafiyar yara ta hanyar ci gaba da shirin rigakafin Sub-National Plus Immunization Days (SNIPDs).

Wannan shiri na da nufin rage yawaitar cututtuka da ke addabar yara ‘yan ƙasa da shekaru biyar, tare da cike gibin kariya daga cututtuka masu yaɗuwa.

Da yake jawabi a wani taro da manema labarai a Yola, Dr. Jacobs Vasumu ya bayyana cewa zagaye na biyu na rigakafin zai gudana daga ranar 2 zuwa 5 ga watan Mayu, tare da ƙarin kwanaki biyu na gyaran aiki.

Ya ce wannan zagaye zai ginu kan nasarorin da aka samu a zagayen farko, domin tabbatar da cewa an kai ga dukkan yaran da suka cancanta ba tare da an bar kowa a baya ba.

A cewarsa, jihar na da burin kai wa yara 1,301,795 masu shekaru daga haihuwa zuwa watanni 59 rigakafi, tare da tanadar allurai sama da miliyan 1.5 domin tabbatar da wadatar su har ma da ƙarin yara da za su iya shiga cikin shirin.

Ya jaddada cewa wannan tsari yana taimakawa wajen ɗaukar matakan kariya ga sabbin haihuwa da kuma baƙi da ke shigowa jihar a lokacin shirin.

Dr. Vasumu ya kuma bayyana cewa duk da nasarorin da aka samu, ana fuskantar ƙalubale kamar gajiyar ma’aikatan lafiya da tsananin zafi, amma ana ɗaukar matakan tabbatar da ingancin allurar ta hanyar tsarin wajen adana sanyi.

Ya ƙara da cewa wayar da kan al’umma da haɗin kan shugabannin gargajiya da na addini sun taimaka wajen rage ƙin karɓar rigakafi, tare da ba da tabbacin cewa jihar za ta amfana da allurar zazzabin cizon sauro nan gaba idan an samu wadatarta a ƙasa baki ɗaya.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *