‘Jarumai na gaskiya’ – Matar Tinubu na taya murnar ranar malamai, ta bukaci a dauki mataki kan karancin su

Uwargidan shugaban Najeriya, Sanata Oluremi Tinubu ta ce malaman makarantu mutane masu daraja da suka cancanci yabo da ƙarƙafa gwiwa.
Remi ta bayyana haka ne a cikin wata sanarwa da fitar domin murnar Ranar Malamai ta bana, inda ta yi kira da a ƙara ɗaukar malamai domin ɗalibai su samu ilimi mai inganci, sannan a kula sosai da haƙƙoƙinsu.
A cewarta, “malamai gwaraza ne gaskiya da suke taimakawa wajen inganta rayuwar al’umma da ma gyara ƙasa.”
“Ƙarancin malamai matsala ce da ke buƙatar ɗauki na gaggawa domin idan aka ƙarfafa malamai ne wasu ma za su yi sha’awar shiga aikin mai matuƙar daraja.”
Ta ƙara da cewa, “a matsayina na tsohuwar malama, ina yabawa da ƙoƙarinku a wannan rana mai muhimmanci ta malamai.”

Hi, it’s Jayrn.
Want to find “hidden money” in your business? Dan shares exactly how to exponentially increase your cashflow and the value of your company with these 5 Key Strategies.
Find out how to find your customer “trigger points” so you know how to market and sell to them. And the best part is… it’s way easier than you think!
Learn More: https://marketersmentor.com/hidden-money.php?refer=tambari.online
Jayrn
Unsubscribe:
https://marketersmentor.com/unsubscribe.php?d=tambari.online