Kotu ta bai wa Sowore belin Naira Miliyan 200 a shari’ar bata sunan Tinubu

0
Kotu ta bai wa Sowore belin Naira Miliyan 200 a shari'ar bata sunan Tinubu

Kotu ta bai wa Sowore belin Naira Miliyan 200 a shari'ar bata sunan Tinubu

Spread the love

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta bai wa ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar AAC, Omoyele Sowore, belin Naira miliyan 200 a shari’ar da ake yi masa kan zargin ɓata sunan Bola Ahmed Tinubu. Alƙali Mohammed Umar ne ya yanke hukuncin tare da sanya wasu tsauraran sharudda kafin a sako Sowore.

Kotun ta umarci Sowore ya gabatar da mutane biyu da za su tsaya masa, inda ɗaya zai kasance basarake daga garinsu, yayin da ɗayan kuma zai mallaki kadara a Babban Birnin Tarayya, Abuja. Haka kuma an umarci masu tsaya masa su kasance an tantance su kafin belin ya fara aiki.

Bugu da ƙari, kotun ta umurci Sowore ya miƙa fasfo ɗinsa na ƙasa da ƙasa ga mataimakin babban magatakardar kotun har sai an kammala shari’ar. Wannan mataki na daga cikin sharuddan da kotun ta gindaya domin tabbatar da bin doka yayin da ake ci gaba da shari’ar.

Alƙali ya kuma ɗage ci gaba da sauraron shari’ar zuwa ranar 6 ga Yuli, 2026, inda ake sa ran Sowore zai fara kare kansa kan zarge-zargen da ake masa.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *