Ribadu ya kalubalanci El-rufa’i da ya kai shaidar sayan sinadari mai guba ga DSS

Ofishin mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu ya mayar da martini ga tsohon gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufai wanda ya nemi bahasi kan shiga da wata guba mai haɗari cikin ƙasar.
Tsohon gwamnan jihar Kaduna, ya zargi ofishin mai bai wa shugaban Najeriya shawara kan harkokin tsaro, a ƙaƙashin jagorancin Mallam Nuhu Ribadu, da sayo kimanin kilogiram 10 na wani sinadari mai haɗari da ake kira ‘thallium sulphate’, daga ƙasar Poland.
El-Rufai ya yi wannan zargin ne a cikin wata wasiƙa da ya aike wa ofishin Ribadu, wadda kuma ya wallafa a shafinsa na X, inda ya ce jagororin adawar ƙasar na neman ƙarin haske game da wannan batun.
