Hukumar NECO ta fitar da sakamakon jarrabawar SSCE ta 2025 a ranar talata

0
1000506276
Spread the love

Hukumar shirya jarrabawa ta Ƙasa ta fitar da sakamakon Jarrabawar Sakandare ta daliban da suka rubuta daga wajen makaranta ta 2025 a ranar Talata, 3 ga Fabrairu, 2026.

An bayyana wannan a cikin wata sanarwa wacce Mukaddashin Daraktan Labarai da Hulɗa da Jama’a na hukumar ya sanya wa hannu a ranar Talata.

A cewar sanarwar, Magatakarda kuma Babban Jami’in Gudanarwa na NECO, Farfesa Dantani Ibrahim Wushishi, ya bada umurnin fitar da sakamakon a hukumance da ƙarfe 10:45 na safe.

Jarabawar ta ‘yan daliban waje na SSCE galibi na dalibai ne masu zaman kansu waɗanda ke neman takardar shaida a wajen tsarin makarantu na yau da kullun.

NECO yawanci tana gudanar da jarrabawar waje don samar da dama ga waɗanda suka rasa takardun su ko kuma suna buƙatar inganta maki.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *