Malamin addinin Musulunci Sheikh ‘Rigi-Rigi’ Kusfa ya rasu yana da shekaru 57

0
1000503155
Spread the love

Shahararren malamin addinin Musulunci a Zariya, Jihar Kaduna, Sheikh Usman Idris Kusfa, wanda aka fi sani da “Rigi-Rigi,” ya rasu yana da shekaru 57.

Wani babban almajirin malamin, Nasiruddeen Umar, wanda aka fi sani da Baharu, ya bayyana hakan ga Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya a ranar Litinin a Zariya.

Umar ya ce Sheikh Kusfa ya rasu da sanyin safiyar Litinin a wani asibiti mai zaman kansa da ke Kaduna bayan ya yi fama da rashin lafiya na tsawon watanni.

A cewarsa, Kusfa ya shahara sosai da koyarwar addinin Musulunci kuma ya samu karbuwa sosai a TikTok da sauran dandamalin sada zumunta.Ya ce malamin ya rasu ya bar mata hudu, ‘ya’ya 37, da jikoki da yawa.

Umar ya kara da cewa an shirya yin jana’izar marigayin a Kusfa, birnin Zariya, da karfe 4:30 na yamma a ranar Litinin.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *