Abba na kan turbar komawa wa’adi na biyu – Ganduje

0
1000486593
Spread the love

Tsohon shugaban jam’iyyar APC na ƙasa kuma tsohon gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana cewa gwamnan Kano “Abba Kabir Yusuf na kan turbar komawa wa’adi na biyu” a zaɓen shekarar 2027.

Ganduje ya bayyana hakan ne a wani saƙo da ya wallafa a shafin sada zumunta na X, inda ya yaba da matakin gwamnan na sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC.

Ganduje ya ce shigowar gwamna Abba cikin APC zai ƙara ƙarfafa jam’iyyar a jihar Kano da ma Arewa gaba ɗaya, yana mai jaddada cewa haɗin kan manyan jagororin jam’iyyar zai taimaka wajen tabbatar da nasara a zaɓuka masu zuwa.

A jiya Litinin ne dai Gwamna Yusuf ya kammala komawa jam’iyyar APC a hukumance, bayan watanni na raɗe-raɗin siyasa da hasashe kan makomarsa.

An gudanar da taron sauya sear gwamnan a wani ƙwarya-ƙwaryan biki da aka shirya a gidan gwamnatin jihar Kano, wanda ya ja hankalin manyan ’yan siyasa da magoya bayan jam’iyyar.

Mahalarta taron sun bayyana komawar gwamnan a matsayin babban sauyi da zai sake fasalta siyasar Kano gabanin zaɓen 2027.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *