Gwamnan Kano ya kai ziyara fadar shugaban ƙasa

0
1000467398
Spread the love

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya kai wa shugaba Bola Tinubu ziyara a fadarsa da ke Abuja.

Gwamnan ya isa fadar shugaban ƙasar ne a yammacin yau Litinin.

Ziyarar tasa na zuwa ne a daidai lokacin da rahotanni ke ƙara tabbata na sauya sheƙarsa daga jam’iyyar NNPP zuwa jam’iyya mai mulki ta APC.

Siyasar Kano ta shiga ruɗani a baya bayan-nan bayan rahotannin sauya sheƙar gwamna Yusuf, wani abu da jagororin NNPP da kuma uban jam’iyyar, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso suka nuna adawa a kai.

Lamarin ya janyo saɓani a cikin jam’iyyar, musamman tsakanin magoya bayan gwamnan da kuma waɗanda ke mubaya’a ga tafiyar Kwankwasiyya da Sanata Kwankwaso ya assasa.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *