Rundunar sojin Nijar ta ce ta kashe ƴanbindiga da dama a Tillaberi

0
1000309384
Spread the love

Rundunar sojin Nijar ta sanar da cewa ta halaka yan bindiga da dama a cikin Jihar Tillaberi a ƙarƙashin wani farmaki na musamman da ta kira “Opération Borkono”.

A yayin farmakin ne kuma sojojin suka ƙwato dabbobi da dama da maharan suka yi awon gaba da su yayin hare-haren da suke kai wa garuruwa.

Rundunar ta kuma ce ta tarwatsa wata mahaƙar zinariya da ke zama maɓuyar yan bindiga, inda aka rufe rijiyoyin haƙar zinariyar da maharan ke amfani da su.

Wannan farmaki na zuwa ne a daidai lokacin da Nijar ke fama da matsalar tsaro.

Sojojin sun bayyana cewa irin waɗannan matakai na musamman za su ci gaba don tabbatar da tsaro da kare rayuka da dukiyoyin al’umma.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *