An fara binciken mutuwar matar da aka manta almakashi a cikinta a Kano

0
1000453788
Spread the love

Hukumomin lafiya a jihar Kano sun bayyana cewa sun kafa wani kwamiti na musamman da zai gudanar da bincike kan yadda wata mata ta rasa ranta, bayan an bar almakashi a cikinta a lokacin da aka yi mata tiyata.

Matar ta rasa ranta bayan wani likita ya manta bai cire almakashin da ya yi mata aikin da shi ba.

Dangin matar sun buƙaci a bi musu haƙƙinta tare da ɗaukar matakin da ya dace a kan wanda ya aikata laifin.

Ma’aikatar lafiyar ta tabbatar da cewa sun sami bayanin cewa matar ta rasa ranta, sanadiyar barin almakashi a cikinta bayan kammala yi mata tiyata.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *