Fafaroma ya nuna damuwa da kama shugaban Venezuela

0
1000429009
Spread the love

Fafaroma Leo ya ce dole ne a tabbatar da martabar Venezuela tare da walwalar ƴan ƙasar fiye da komai.

Jagoran ɗariƙar Katolikan na duniya – wanda ya yi aiki na kusan shekara 20 a kudancin Amurka – ya ce yana biye da abubuwan da ke faruwa a Venezuela.

Tun da farko China ta yi kiran a gaggauta sakin Shugaba Maduro, tana mai cewa Amurka ta keta dokokin duniya.

Ana sa ran Mista Maduro zai gurfana a gaban kotu ranar Litinin domin fuskantar tuhume-tuhume kan safarar miyagun ƙwayoyi da makamai, zarge-zargen da a baya ya sha musantawa.

A gobe ne kwamitin tsaro na Majalisar Dinkin Duniya zai yi wani taro domin tattaunawa kan harin da Amurka ta kai wa Venezuela tare da kama shugaban ƙasar da mai ɗakinsa.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *