Dubban mutane sun tsere daga kan Iyakar Thailand da Cambodia bayan sabon rikici

0
1000354938
Spread the love

Dubban mazauna yankunan da ke kan iyakar Thailand da Cambodia sun tsere a ranar Litinin, yayin da wani sabon rikici ya ɓarke, wanda ya yi sanadin mutuwar aƙalla mutum biyar.

Ɓangarorin biyu dai sun ɗora alhakin fara rikicin, lamarin da ya zama mafi muni tun bayan yarjejeniyar tsagaita wuta da suka cimma a watan Yuli.

Tun watan Mayu, tashin hankali tsakanin ƙasashen biyu ya yi sanadin mutuwar fiye da mutum 40, tare da hana shigo da kaya da kuma takaita zirga-zirga.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *