An rantsar da shugaban riƙo a Guinea Bissau

0
1000328080
Spread the love

Sojojin da suka ƙwace mulki a Guinea-Bissau sun rantsar da wani Janar a matsayin sabon shugaban riƙo na tsawon shekara ɗaya.

Janar Horta N’Tam ya sha rantsuwa ne yau alhamis a hedikwatar sojojin da ke babban birnin ƙasar Bissau.

Hakan na zuwa ne bayan da suka hamɓarar da shugaban ƙasar Umaro Sissoco Embalo a jiya Laraba.

Ƙungiyar raya tattalin arziƙin ƙasashen yammacin Afirka ECOWAS ta yi Allawadai da ƙwace mulkin da aka yi, inda ta yi kiran a gaggauta sakin hamɓararren shugaban ƙasar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *