Zan tabbatar da haɗin kan ƴan Kamaru – Paul Biya

0
1000250745
Spread the love

Bayan nasarar da ya samu a karo na takwas, shugaba kasar Kamaru Paul Biya mai kimanin shekaru 92 da haihuwa ya yi alkawarin dawo da hadin kai da zaman lafiya a kasar.

Paul Biya ya kasance a kan mulki tsawon shekaru 42 da suka gabata sannan kuma shi ne shugaban kasa mafi tsufa a duniya.

Babban dan adawar kasar Issa Tchiroma Bakary, ya yi watsi da sakamakon zaben da aka fitar wanda ya janyo tashin hankali, inda ya yi zargin cewa wasu mutane sun kashe masa magoya bayansa biyu a kofar gidansa.

Ƴansanda sun yi amfani da ruwan zafi da kuma hayaki mai sa hawaye wajen tarwatsa masu zanga zanga a Douala.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *