Sojojin Najeriya sun kashe manyan mayaƙan ISWAP

Dakarun rundunar hadin gwiwa ta Operation Haɗin Kai da ke aiki a yankin arewa maso gabshin Najeriya, sun sanar da nasarar kai wasu munanan hare-hare kan ƙungiyoyin ƴan bindiga da ke addabar yankin.
A cikin wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na rundunar, Laftanar Kanar Sani Uba ya fitar, ya ce bayanan sirri sun tabbatar da kashe wani babban kwamandan ƙungiyar ISWAP mai suna Julaibib a yankin Gujba.
A cewarsa, an yi nasarar kashe shugaban mayaƙan na ISWAP ne bayan wanii artabu da aka yi tsakanin mayaƙan da dakarun soji a kusa da garin Kimba da ke ƙaramar hukumar Damboa ta jihar Borno, a ranar 30 ga watan Janairu.
Laftanar kanar Uba ya kuma sanar da cewa rundunar ta yi nasarar kashe wasu ƴan bindiga uku bayan wani harin kwanton ɓauna da aka kai tsakanin Ngazalgana da Lamusheri a jihar Borno.
Ya bayyana cewa, wannan farmakin ya biyo bayan sahihan bayanan sirri ne da aka samu kan kai kawo da ƙungiyoyi masu tayar ƙayar baya ke yi a yankin.
A cewarsa aikin wani bangare ne na ci gaba da ƙoƙarin hana mayakan samun walwala da kuma daƙile ƙarfin gudanar da ayyukansu a duk faɗin yankin.
