Shugaban INEC ya sauka daga muƙaminsa bayan ƙarewar wa’adinsa

0
1000151134
Spread the love

Shugaban hukumar zaɓen Najeriya, Farfesa Mahmood Yakubu ya sauka daga muƙaminsa tare da miƙa ragamar jagorancin hukumar ga May Agbamuche wadda za ta riƙe muƙamin a matsayin riko kafin naɗa sabon shugaba.

Farfesa Yakubu ya bayyana hakan ne ranar Talata a lokacin ganawarsa da kwamishinonin hukumar a shalkwatar zaɓen da ke Abuja.

Agbamuche ita ce wadda ta fi kowa jimawa a matsayin babbar kwamishina a hukumar zaɓen ƙasar.

Ya kuma yi kira da sauran kwamishinoni da daraktocin hukumar su bai wa Agbamuche cikakken goyon bayan kafin lokacin naɗa sabon shugaban hukumar.

A watan Oktoba 2015 ne tsohon Shugaban Najeriya Marigayi, Muhammadu Buhari ya naɗa Farfesa Yakubu a matsayin shugaban hukumar INEC, wanda ya maye gurbin Farfesa Attahiru Jega.

Haka a 2020 Muhammadu Buhari ya sake naɗa shi a karo na biyu don jagorantar hukumar a wa’adi na biyu.

Farfesa Yakubu ya jagoranci hukumar na tsawon shekara 10, tare da gudanar da manyan zabukan kasar biyu na 2019 da 2015.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *