Senata Ndume ya buƙaci Tinubu ya janye sunayen jakadu

Tsohon shugaban masu rinjaye na majalisar dattawan Najeriya, Ali Ndume, ya buƙaci shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya janye jerin sunayen jakadun da ke gaban majalisar a halin yanzu, bisa zargin cewa an saba wa ƙa’idar tsarin tarayya da kundin tsarin mulkin 1999 ya tanada.
A ranar Alhamis ɗin da ta gabata ne majalisar dattawa ta karɓi jerin sunayen waɗanda shugaba Tinubu ke neman ya naɗa, waɗanda aka miƙa wa kwamitin majalisar dattawa kan harkokin ƙasashen waje domin tantance su.
Sai dai Ndume mai wakiltar Borno ta Kudu a wata sanarwa da ya fitar a ranar Asabar ya ce jerin sunayen ya ci karo da sashe na 14(3) na kundin tsarin mulkin ƙasar, wnda ya buƙaci a yi daidaito tsakanin ɓangarorin ƙasar wurin bayar da muƙaimai.
Ya ce yayin da wasu jihohin ke da mutum uku ko huɗu, wasu kuma ba su da ko guda ciki har da jihar Gombe.
