NUJ na jimamin ƴan jarida bakwai da suka mutu a hatsarin mota a Gombe

0
1000416559
Spread the love

Ƙungiyar ƴan jarida ta ƙasa (NUJ) ta bayyana jimami kan mutuwar ’yan jarida bakwai da suka mutu a wani mummunan hatsarin mota da ya faru a jihar Gombe ranar Litinin.

Rahotanni sun ce hatsarin ya auku ne sakamakon fashewar taya, yayin da ’yan jaridar ke dawowa daga ɗaurin aure na wani abokinsu a ƙaramar hukumar Kaltungo.

An tabbatar da cewa mutum huɗu sun jikkata.

Shugaban NUJ na ƙasa, Alhassan Yahya, ya ce rasuwar ta girgiza al’ummar ’yan jarida a Gombe da ma ƙasar baki ɗaya, yana mai bayyana marigayan a matsayin ƙwararrun ma’aikata masu jajircewa da gaskiya.

Ya miƙa ta’aziyya ga iyalan mamatan tare da kira da a ƙara tsaurara matakan tsaro a kan hanya domin hana asarar rayuka.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *