NBA ta nemi a dakatar da aiwatar da sabuwar dokar haraji

Ƙungiyar Lauyoyin Najeriya (NBA) ta yi kira da a dakatar da aiwatar da sabuwar dokar haraji da ake shirin fara aiki da ita a ranar 1 ga watan Janairun 2026.
Wannan dai na zuwa ne bayan zargin cewa an sauya ko kuma yin cushe a dokar da aka fitar saɓanin abin da majalisar ƙasar ta amince da shi.
Wannan batu ya fara fitowa ne makon da ya gabata bayan wani ɗan majalisar wakilai daga Sokoto, Abdulsamad Dasuki, ya bayyana cewa akwai bambance-bambancen a dokar da ya lura da su.
A wata sanarwa da ta fitar ranar Talata, NBA ta ce lamarin na tayar da “hankali dangane da sahihanci da gaskiya da amincin tsarin dokokin Najeriya.”
