Najeriya ta tabbatar da zuwan sojojin Amurka ƙasar

0
1000500636
Spread the love

Ministan tsaron Najeriya, Janar Christopher Musa, ya tabbatar wa BBC cewa wata ƙaramar tawagar sojojin Amurka tana aiki a cikin ƙasar.

Ya ce sojojin na Amurka za su kasance suna bayar da horo ga sojojin Najeriya domin shiryasu wajen gudanar da ayyuka.

Ministan bai bayyana yawan sojojin ba, ko lokacin da suka isa ƙasar, ko inda aka jibge su, ko tsawon lokacin da za su zauna a Najeriya ba.

Sojojin Amurka da na Najeriya sun shafe shekaru masu yawa suna gudanar da bayar da horo na haɗin gwiwa, da nufin ƙarfafa ƙwarewar Najeriya a fannin tattara bayanan sirri da yaƙi da ta’addanci.

Shugaban sojin Amurka a Afirka AFRICOM, Janar Dagvin R. M. Anderson, ya shaida wa manema labarai a ranar Talata cewa tura sojojin Amurka zuwa Najeriya ya kasance ne bisa buƙatar gwamnatin Najeriya, kuma hankalinsu ya ta’allaka ne kan tallafi wajen tattara bayanan sirri.

Najeriya ta ƙara haɗin gwiwa da Amurka ne a daidai lokacin da take fuskantar manyan ƙalubalen tsaro, ciki har da hare-haren ‘yanbindiga da sace-sacen mutane don neman kuɗin fansa, da yaɗuwar ‘yan bindiga.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *