Mun bai wa Iran kwana 10 ko su amince da yarjejeniya ko su gani a ƙwaryarsu – Trump

0
1000440396
Spread the love

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya bayyana cewa Amurka ta bai wa Iran wa’adin kwanaki 10 don su amince da yarjejeniya kan shirinta na nukiliya, in ba haka ba Amurka za ta ɗauki matakin soja, kuma duniya za ta san abin da zai faru.

A taron farko na shirin samar da zaman lafiya da ya jagoranta a Washington DC, Trump ya ce a tattaunawar da ake yi da Iran: “Dole ne mu cimma yarjejeniya mai ma’ana, in ba haka ba abubuwa masu muni za su faru.”

A ‘yan kwanakin nan, Amurka ta ƙara tura sojoji zuwa Gabas ta Tsakiya, yayin da aka samu rahotanni na ci gaban tattaunawa tsakanin wakilan Amurka da Iran a Switzerland.

‘Yan majalisar dokoki na jam’iyyar Democrats da wasu na jam’iyyar Republicans sun nuna rashin amincewa da duk wani matakin soja a Iran ba tare da izinin majalisa ba.

Gwamnatin Iran ta shaida wa Babban Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya cewa za ta ɗauki sansanonin soja na Amurka a yankin a matsayin wuraren hari idan kai hari kan Iran.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *