Kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar da hukuncin kisa kan Abdulmalik Tanko da ya kashe Hanifa

Kotun ɗaukaka ƙara ta tabbatar da hukuncin kisa da babbar kotu ta yanke a kan Abdulmalik Tanko, wanda aka samu da laifin sacewa tare da kashe ƙaramar yarinya Hanifa Abubakar.
Hukuncin ya biyo bayan shari’ar da ta ja hankalin al’umma baki, inda kotu ta same shi da laifin aikata kisan.
Wannan mataki, a cewar gwamnatin jihar Kano, wata babbar nasara ce domin tabbatar da adalci, wanda ke ƙarfafa gwiwar mutane domin su ƙara al’umma da ɓangaren, tare da tabbatar da cewa waɗanda suka aikata manyan laifuka, musamman waɗanda suka shafi kisan yara, ba za su tafi a banza ba.
Sanarwar tabbatar da hukuncin na ɗauke ne a wani rubutu da babban lauyan jihar kuma kwamishinan shari’a, Abdulkarim Kabiru Maude ya sanar, inda ya yaba da hukuncin yana mai cewa hakan ya nuna ƙarfin doka da jajircewar ɓangaren shari’a wajen kare rayuka, musamman na yara da sauran masu rauni a cikin al’umma.
