INEC ta gargaɗi masu sayen ƙuri’a a zaben Abuja
Hukumar zaɓen Najeriya INEC ta gargaɗi masu sayen ƙuri’a a zaɓukan Abuja.
Cikin wata sanarwa da hukumar ta wallafa a shafinta na X, ta wallafa lambobin wayar da za a sanar da ita a duk wurin da aka ga hakan na faruwa.
Ana gudanar zaɓukan shugabannin ƙananna hukukomin birnin shida da kansiloli 62.INEC ta ce akwai rumfunan zaɓe 2,822 a birnin Abuja.
A cewar hukumar zaɓen fiye da mutum miliyan 1.6 ne suka yi rajistar zaɓe a birnin.
