Hukumar NECO ta fitar da sakamakon jarrabawar SSCE ta 2025 a ranar talata

Hukumar shirya jarrabawa ta Ƙasa ta fitar da sakamakon Jarrabawar Sakandare ta daliban da suka rubuta daga wajen makaranta ta 2025 a ranar Talata, 3 ga Fabrairu, 2026.
An bayyana wannan a cikin wata sanarwa wacce Mukaddashin Daraktan Labarai da Hulɗa da Jama’a na hukumar ya sanya wa hannu a ranar Talata.
A cewar sanarwar, Magatakarda kuma Babban Jami’in Gudanarwa na NECO, Farfesa Dantani Ibrahim Wushishi, ya bada umurnin fitar da sakamakon a hukumance da ƙarfe 10:45 na safe.
Jarabawar ta ‘yan daliban waje na SSCE galibi na dalibai ne masu zaman kansu waɗanda ke neman takardar shaida a wajen tsarin makarantu na yau da kullun.
NECO yawanci tana gudanar da jarrabawar waje don samar da dama ga waɗanda suka rasa takardun su ko kuma suna buƙatar inganta maki.
