Gwamnatin Nijar ta ƙwace mahaƙar zinare daga kamfanin Australia

Gwamnatin soji a Nijar ta ƙwace katafaren cibiyar mahaƙar zinare ɗaya tilo da ke ƙasar, bayan ta zargi Kamfanin Australia da ke tafiyar da harkokin cibiyar da saɓa dokoki.
Kamfanin McKinel na Australia ke tafiyar da harkokin mahakar tun 2019.
Amma gwamnatin sojin da ta ƙwace mulki shekaru biyu da suka gabata, ta ce McKinel ya gaza wajen tabbatar da shirin zuba jari na dala miliyan 10 yanayin da ya jefa mahaƙar cikin barazanar tattalin arziki.
Ko a watan Yuni wannan shekarar sai da gwamnatin Sojin ƙasar ta ƙwace harkar tafiyar da Uranium na Orano daga hannun Faransa.
