Gwamnatin Najeriya ta ayyana masu sace mutane a matsayin ’yan ta’adda

0
1000392650
Spread the love

Gwamnatin Najeriya ta ayyana masu garkuwa da mutane da ƙungiyoyi masu ɗaukar makamai da masu tayar da ƙayar baya a matsayin ’yan ta’adda, a wani sabon mataki da nufin ƙara tsaurara yaƙi da sace-sacen mutane da hare-hare da kuma tashin hankali a yankunan karkara.

Ministan yaɗa labarai, Mohammed Idris ne ya bayyana hakan a taron manema labarai na ƙarshen shekara da aka gudanar a Abuja, inda ya ce matakin ya kawo ƙarshen ruɗani kan yadda ake kallon irin waɗannan laifuka.

Ya ce daga yanzu duk wanda ya sace mutane ko kuma ya kai hari kan manoma ko ya tsoratar da al’umma, za a ɗauke shi a matsayin ɗan ta’adda, kuma za a yi mu’amala da shi bisa haka.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *