Dakarun Najeriya na fiskantar matsaloli na rashin samun walwala – Lt Oluyede.

0
1000044268
Spread the love

Babban hafsan sojin ƙasa na Najeriya, Laftanar Janar Olufemi Oluyede ya yi kiran ƙara wa rundunarsa kuɗi domin tabbatar da ayyuka da walwalar dakarun rundunarsa.

Janar Oluyede ya bayyana hakan ne lokacin ganawa da kwamitin majalisar dattawan ƙasar kan sojojin ƙasa a lokacin wata ziyara da tawagar kwamitin ya kai shalkwatar sojojin ƙasa na ƙasar da ke Abuja.

Baban hafsan ya yaba wa ayyuka da taimakon da kwamitin majalisar dattawan ke bai wa rundunarsa.

Sai dai ya sake jaddada cewa kuɗin da ake ware wa rundunar ba sa biya wa rundunar buƙatunta, kamar yadda rudunar ta wallafa a shafinta na X.

Janar Oluyede ya kuma bayanin wasu manyan matsalolin da rundunar ke fuskanta, musamman wajen gudanar da ayyukanta da ƙarancin muhalli ga dakarun rundunar.

Haka kuma ya yi kira ga ƴan majalisar su su duba yiwuwar ƙara wa rundunar ƙudi a kasafin kuɗi domin magance matsalolin da take fuskanta.

Shugaban kwamitin majalisar dattawan, Sanata Abdulaziz Yar’Adua ya yaba wa rundunar sojin ƙasan kan jajircewar da suke yi wajen samar da tsaro a faɗin ƙasar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *