APC ta lashe zaɓukan cike gurbin Kano

0
20260222_154009
Spread the love

Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta samu nasara a zaɓen cike gurbi na mazaɓar Ungogo da Kano Municipal a majalisar dokokin jihar Kano.

Gidan Talbijin na Ƙasar NTA ya ruwaito cewa a karamar hukumar Kano Municipal ɗan takarar jam’iyyar APC, Aliyu Nabil Daneji, ya samu nasara da ƙuri’u 7,484.

Jami’in tattara sakmakon zaɓen Farfesa Ibrahim Tajo Siraj ne ya bayyana sakamakon zaɓen tare da ayyana shi a matsayin wanda aka zaɓa.

Hakazalika, a mazaɓar Ungogo, ɗan takarar jam’iyyar APC, Aminu Sa’ad, ya samu nasara ne bayan ya samu ƙuri’u 8,975. Jami’in tattara sakmakon zaɓe, Farfesa Ali Tijjani Abdullahi, ya bayyana sakamakon zaɓen tare da ayyana shi a matsayin wanda ya lashe kujerar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *