Ana barazanar zuwa kotu kan batun kafa Hisbah mai zaman kanta a Kano

0
1000364823
Spread the love

Yunkurin tsohon gwamnan Kano, Dr Abdullahi Umar Ganduje, na kafa wata kungiyar Hisbah mai zaman kanta na ci gaba da haifar da ce-ce-ku-ce a jihar Kano da ke arewa maso yammacin Najeriya, inda wasu daga cikin ’yan siyasa da al’umma ke barazanar kai maganar gaban kotu

Masu sukar tsarin na ganin cewa yunƙurin na iya janyo tashin hankali, duba da yadda ake fassara ikon rundunar Hisbah a Kano a matsayin wanda doka ta tanada.

Tsohon ɗan takarar gwamna, Ibrahim Al-Amin Little, ya kasance cikin masu adawa da shirin, inda ya gargaɗi Ganduje da ya janye wannan batu na kafa Hibah mai zaman kanta.

Ya ce kafa irin wannan ƙungiya zai buɗe ƙofa ga wasu su fara ƙirƙiro nasu, lamarin da zai iya rikitar da harkokin tsaro.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *