An rantsar da shugaban riƙo a Guinea Bissau

Sojojin da suka ƙwace mulki a Guinea-Bissau sun rantsar da wani Janar a matsayin sabon shugaban riƙo na tsawon shekara ɗaya.
Janar Horta N’Tam ya sha rantsuwa ne yau alhamis a hedikwatar sojojin da ke babban birnin ƙasar Bissau.
Hakan na zuwa ne bayan da suka hamɓarar da shugaban ƙasar Umaro Sissoco Embalo a jiya Laraba.
Ƙungiyar raya tattalin arziƙin ƙasashen yammacin Afirka ECOWAS ta yi Allawadai da ƙwace mulkin da aka yi, inda ta yi kiran a gaggauta sakin hamɓararren shugaban ƙasar.
