An kammala taron hafsoshin tsaron Afrika

Shugabannin sojin Afrika sun kammala wani taro na ƙoli a Abuja wanda ya mayar da hankali kan yawaitar matsalolin tsaro a nahiyar.
Shugabannin tsaro daga ƙasashe irin su Nijar da Somaliya da Ghana da Masar sun hallara a babban birnin Najeriya domin tattaunawa kan dabarun zaman lafiya da tsaro na cikin gida.
An kammala wannan taro mai tsawon kwanaki uku a ranar Laraba.
Mataimakin shugaban Najeriya, Kashim Shettima ne ya yi jawabi ga mahalarta a lokacin buɗe taron, inda ya buƙaci kasashen Afrika su zama masu fito da sabbin fasahohi a fannin tsaro, tare da gargadin cewa dogaro da hanyoyin waje ba zai dore ba.
