Adamawa: Sabon kwamishinan ƴan sanda ya kama aiki

0
IMG-20260327-WA0035

Sabon kwamishinan ƴan sanda na Adamawa

Spread the love

Sabon Kwamishinan ‘Yan Sanda na Jihar Adamawa, CP Kabir Umar Hassan, ya kama aiki a ranar 27 ga Maris, 2026 a matsayin kwamishina na 33 na rundunar ƴan sanda a jihar.

CP Hassan gogaggen jami’i ne da ya shafe shekaru yana aiki a fannoni daban-daban da suka haɗa da bincike, gudanarwa da ayyukan tsaro a sassa daban-daban na Najeriya.

Kafin wannan muƙami, ya kasance Kwamishinan ‘Yan Sanda a hedikwatar rundunar da ke Legas.

Rundunar ‘yan sandan jihar ta buƙaci jama’a da su ci gaba da ba da haɗin kai da sahihan bayanai domin inganta tsaro a jihar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *