An rantsar da Samia Saluhu Hassan a wa’adin mulkin Tanzaniya na biyu

0
1000258029
Spread the love

An rantsar da Shugaba Samia Suluhu Hassan a wa’adin mullki na biyu a matsayin shugabar Tanzaniya.

Cikin wani ƙwarya-ƙwaryar biki da aka gudanar cikin tsaurara matakan tsario a Dodoma, babban birnin ƙasar an rantsar da shugabar a wani wurin da ba a bar mutane da dama sun halarta ba.

Baƙin da aka gayyata ne kawai aka bai wa damar zuwa wurin, yayin da ake ci gaba da zaman ɗar-ɗar a ƙasar, sakamakon rikicn zaɓe da aka samu a ƴankwanakin nan.

Shugaba Samia ta lashe zaɓen da aka gudanar a makon da ya gabata da kashi 98 cikin 100 na ƙuri’un da aka kaɗa.

Sai dai ƴan hamayya sun yi watsi da sakamakon a matsayin magudi.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *