Najeriya na sa ran haƙo gangan ɗanyen mai miliyan1.8 a kullum

0
1000204872
Spread the love

Shugaban kamfanin mai na Najeriya, NNPCL, Bayo Ojulari, ya bayyana kyakkyawan fatan cewa ƙasar zata dinga haƙo gangan ɗanyen mai miliyan1.8 kafin ƙarshen shekarar 2025.

Kafar watsa labarai ta Channels TV ta ce shugaban kamfanin ya bayyana hakan ne a ranar Lahadi, yayin da ya ke sanar da shugaba Bola Tinubu kan ayyukan kamfanin a jihar Legas.

Mista Ojulari ya ce gyare-gyaren da suka yi a watannin Agusta da Satumba zasu taimaka wurin samar da ci gaba a wannan watan.

Inda ya ƙara da cewa “Muna fatan kafin ƙarshen shekarar nan mu kai ga haƙo aƙalla gangan ɗanyen mai miliyan ɗaya da dubu 800 a kullum. ”

A halin yanzu dai ƙasar na haƙo ganga miliyan 1.71 a kullum.

Kuma ta kasance ɗaya daga cikin ƙasashen da ke gaba-gaba wurin samar da ɗanyen mai a ƙungiyar OPEC a duniya.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *