Hukumar EFCC ta kama wasu mutane 42 da ake zargi da damfarar Intanet a Gashua

0
1000196781
Spread the love

Jami’an hukumar shiyyar Maiduguri na hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC sun kama wasu mutane 42 da ake zargi da damfarar yanar gizo a karamar hukumar Gashua ta jihar Yobe.

An kama su ne a wani samame da aka kai ranar Laraba, 1 ga Oktoba, 2025 a wurare daban-daban a cikin Gashua, biyo bayan sahihan bayanan sirri kan yadda suke da hannu a laifukan da suka shafi kwamfuta.

Kayayyakin da aka kwato daga hannunsu sun hada da babura bakwai, motar Mercedes Benz daya, wayoyi hamsin da biyar (55) da kwamfutoci, da kuma playstation 5 (PS5) da playstation 4 (PS4) consoles.

Bayanan sirri da Hukumar ta samu na alakanta wadanda ake zargin da zamba daban-daban da suka shafi intanet.

Za a gurfanar da su gaban kotu da zarar an kammala bincike.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *