Shettima ya gana da shugaban MDD kan sama wa Najeriya kujerar dindindin

0
1000183803
Spread the love

Mataimakin shugaban Najeriya Kashim Shettima ya gana da babban sakataren Janar na Majalisar Dinkin Duniya, António Guterres a shalkwatar majalisar da ke Amurka.

Cikin wata sanarwa da ofishin Shettiman ta fitar ta ce shugabannin biyu sun tattauna batutuwa da dama masu muhimmai ciki har da ƙudirin Najeriya na samun kujerar dindindin a Majalisar Dinkin Duniya.

A lokacin ganawar, Shettima ya ƙarfafa buƙatar Najeriya na neman goyon bayan Majalisar Dinkin Duniyar don cimma ƙudirin nata na samun kujerar dindindin a kwamitin tsaro na majalisar.

Shugabannin sun kuma tattauna batutuwan ƙarfafa cimma muradun ƙarni, da sauyin yanayi da ƙararra dimokradiyya a Najeriya da ma yankin Afirka.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *