Ma’aikatan lantarki sun fara yajin aiki a Najeriya

0
1000181345
Spread the love

Ƙungiyar ma’aikatan wutar lantarki ta ƙasa a Najeriya (NUEE) ta umarci dukkan mambobinta da su dakatar da aiki nan take, kamar yadda ta bayyana cikin wata sanarwa da ta fitar.

Matakin ya janyo fargaba kan yiwuwar katsewar lantarki a sassan ƙasar, musamman a wuraren da aka samu ci gaba wajen samun wutar tun bayan ƙara kuɗi a shekarar da ta gabata.

Ƙungiyar ta bayyana dalilan yajin aikin da suka haɗa da rashin biyan albashi tun daga watan Afrilun 2025, da gazawar gwamnati wajen aiwatar da mafi ƙarancin albashi da rashin kayan aiki da na kariya, da kuma rashin biyan hakkokin fansho.

Haka kuma ta koka da yadda aka ci gaba da riƙe ma’aikata a matsayin na ɗan lokaci ba tare da daidaita matsayinsu ba.

Sakamakon wannan yajin aiki, jama’a na iya fuskantar matsalolin samar da wuta, inda ake hasashen wutar za ta ragu ko ta daina samuwa gaba ɗaya a wasu wurare.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *