Gwamnatin Najeriya za ta sasanta rikici tsakanin jihohi da kamfanonin lantarki

Yayin da rikici ke ƙara taɓarɓarewa tsakanin jihohi da kamfanonin rarraba wuta (Discos) kan wanda ke da ikon tsara farashin wutar lantarki, gwamnatin ta shiga tsakani ta hanyar hukumar kula da wutar lantarki ta Najeriya (NERC), inda ta gayyaci duk masu ruwa da tsaki zuwa taro a mako mai zuwa a Legas domin sasanta rikicin kamar yadda jaridar PUNCH ta ruwaito.
Kwamishinonin makamashi na jihohi sun jaddada cewa dokar wutar lantarki ta 2023 ta ba su ikon tsara kasuwannin wuta a yankunansu.
Amma kamfanonin rarraba wutar lantarki sun yi iƙirarin cewa, duk da cewa dokar ta ba jihohi damar tsara kasuwannin wutar lantarki, ba su da ikon sanya farashin wutar da ke ketare iyakokin jihohi.
Sakamakon haka, babu jihohi ko Discos da suke son sassauta matsayinsu kan wanda ke da ikon tsara farashin wutar lantarki.
