Cutar kwalara ta hallaka mutum 8 a Zamfara

Ɓarkewar cutar cholera a gundumar Bukkuyum da ke jihar Zamfara a arewa maso yammacin Najeriya, ta yi sanadin mutuwar aƙalla mutum takwas.
Cutar ta kuma kama fiye da mutum 200 a cikin ƙauyuka 11, kamar yadda mazauna yankin da hukumomin ƙasa suka tabbatar a ranar Alhamis.
Cutar kwalara cuta ce da ke yaɗuwa ta hanyar ruwa a Najeriya, inda hukumomin lafiya ke danganta yawaitar ta da ƙarancin tsaftataccen ruwa musamman a yankunan karkara da kuma unguwannin marasa galihu a birane.
