Abinci na dab da kare mana a Najeriya – Save the Children

Wata ƙungiyar kare yara ta Save the children ta ce aƙalla ƙasashe huɗu a Afirka, ciki har da Najeriya da Kenya, Somalia da Kudancin Sudan na iya fuskantar ƙarewar abincin tamowa a cikin watanni uku masu zuwa idan ba a samu ƙarin taimako ba, lamarin da ke sanya yara masu ƙarancin abinci mai gina jiki cikin haɗarin mutuwa.
A cikin shekaru 30 da suka gabata, wannan abincin gaggawa ya ceci rayukan miliyoyin yara masu ƙarancin abinci mai gina jiki.
Yaro mai ƙarancin abinci mai gina jiki sosai yana cikin haɗarin mutuwa sau tara fiye da yaron da ke da lafiya idan suka kamu da cututtuka na yau da kullum.
A Najeriya, yara kusan miliyan 3.5 da ke ƙasa da shekaru biyar suna fama da ƙarancin abinci mai gina jiki mai tsanani musamman a arewa maso gabas da arewa maso yamma, kuma suna cikin haɗarin mutuwa idan ba a basu kulawa da abincin da ya kamata ba da wuri.
Najeriya na buƙatar aƙalla kwalayen abincin tamowa 629,000 domin kula da waɗannan yara, amma har yanzu kaso 64 kacal aka samo.
A Kenya, musamman a Turkana, yara na ƙara fuskantar matsalar ƙarancin abinci mai gina jiki da rashin tsaro na abinci saboda fari da ambaliyar ruwa da ake fuskanta.
