‘Yan bindiga sun kashe mutum uku, tare da garkuwa da dayawa a wani sabon hari da suka kai a Katsina.

0
1000050013
Spread the love

Wasu ‘yan bindiga dauke da makamai sun kashe mutane uku tare da yin garkuwa da wasu da dama a wasu hare-hare da suka kai wasu kauyuka biyu a karamar hukumar Malumfashi ta jihar Katsina.

Hare-haren, wadanda suka faru a ranar Juma’a, an bayar da rahoton ne a wani sako a shafin X ta wani mai sharhi kan harkokin tsaro Bakatsine a ranar Asabar.

A cewar sanarwar, lamarin na farko ya faru ne a unguwar Karfi jim kadan bayan sallar Juma’a. Maharan sun kashe mutum daya sannan wasu biyu suka tafi da su.

Bayan sa’o’i kadan, ‘yan fashin sun sake kai hari a wannan karon a Layin Minister.

An kashe mutane biyu, wasu da dama kuma sun jikkata, an kuma yi awon gaba da mazauna yankin da dama a harin na biyu.

Har yanzu dai hukumomi ba su fitar da wata sanarwa a hukumance kan lamarin ba.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *