Zan ci gaba da dagewa har sai na yi nasara kan shugaba Biya – Issa Tchiroma

Ɗan takarar jam’iyyar adawa a Kamaru Issa Tchiroma ya sha alwashin ci gaba da dagewa har sai ya yi nasara kan Shugaba Paul Biya yana mai cewa shi ne ya samu yawan ƙuri’u a zaɓen..
Tchiroma ya kuma yi kira ga magoya bayansa da su ci gaba da zanga-zangar nuna rashin amincewa da sakamakon zaben da ya bayyana Paul Biya a matsayin wanda ya ci zaɓen.
Wannan na zuwa ne yayin da wata ƙungiyar al’umma ta yi Allah wadai da mutuwar mutane da kama-karya da aka yi yayin zanga-zanga a birane da dama na ƙasar.
Shugaba Paul Biya, wanda shi ne tsohon shugaban ƙasa mafi tsufa a duniya mai shekaru 92, yana mulkin Kamaru tun shekarar 1982.
Zaben ranar 12 ga Oktoba da aka bayyana sakamako a ranar Litinin ya ƙara jefa ƙasar cikin tashin hankali, yayin da masu sukar Biya ke zarginsa da amfani da hukumomin gwamnati wajen riƙe mulki da ƙarfi da karfe.
