2027: Tinubu zai sha kaye idan Atiku da Jonathan suka fafata – Olarewaju

0
1000202626
Spread the love

Babban mai taimaka wa tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar kan harkokin siyasa, Demola Olarewaju, ya ba da shawarar yadda shugaba Bola Tinubu zai fadi zaben shugaban kasa a 2027.

Olarewaju ya bayyana cewa idan Atiku da tsohon shugaban kasa Goodluck Jonathan suka fito takarar shugaban kasa a jam’iyyu daban-daban a 2027, Tinubu zai fadi zabe.

Da yake amsa tambayoyi a kafar Mic On podcast a ranar Asabar, Olarewaju ya ce Jonathan zai samu goyon bayan mutane idan ya lashe zaɓen fidda gwani na firamare.

Da aka tambaye shi ko Jonathan zai fito a dandalin PDP, Atiku kuma ya fito a dandalin ADC, me zai faru da Tinubu, sai ya amsa da cewa: “APC zata sha kaye, APC ba za ta samu gindin zama ba a (zaben 2027) idan Jonathan ya fito a PDP, Atiku ko wani ya fito a ADC.”

Ya kuma jaddada cewa jam’iyyar PDP ba ta da karfi a siyasar kasa yanzu.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *