Kashim Shettima zai yi wa taron MDD jawabi a yau

0
1000178743
Spread the love

Nan gaba a yau Mataimakin Shugaban Najeriya Kashim Shettima zai gabatar da jawabin ƙasar a babban taron Majalisar Ɗinkin Duniya (UNGA) da ke gudana a birnin New York na Amurka.

Ana sa rana Shettima zai gabatar da jawabin a madadin Shugaba Bola Tinubu a tsakanin ƙarfe 3:00 na rana zuwa 9:00 na dare agogon New York a taron wanda shi ne karon 80.

Fadar shugaban Najeriya ba ta fayyace abin da Shettima zai tattauna a kai ba, amma akwai yiwuwar zai jaddada kiran a bai wa nahiyar Afirka kujerar dindindin a Kwamatin Tsaro na MDD kamar yadda ya yi a shekarar da ta gabata.

Bayan haka mataimakin shugaban ƙasar zai gana da takwarorinsa na ƙasashen dunya, inda tun a jiya Talata ya tattauna da shugabar Namibia Nandi-Ndaitbia.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *