Majalisar dokoki ta buɗe ofishin Sanata Natasha

0
1000176327
Spread the love

Majalisar Dokoki ta buɗe ofishin Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan da ke Suite 2.05 a sashen Majalisar Dattawa.

Sanatar mai wakiltar Kogi ta Tsakiya ta rubuta wa Majalisar Dattawa mako guda da ya wuce domin sanar da niyyarta ta komawa aiki bayan dakatarwa na tsawon watanni shida.

A watan Fabrairu ne dai tankiya ta ɓarke a zauren majalisar dattawa tsakanin shugaban majalisar, Godswill Akpabio da Sanata Natasha al’amarin dai ya kai ga har Akpabio ya umarci ɗaya daga cikin masu yi wa sandan majalisar hidima da ya fitar da ita daga zauren majalisar lamarin da ya kai ga dakatar da ita na tsawon wata shida.

Wannan lamarin ya kai ga har Sanata Natasha ta yi kira ga Majalisar Ɗinkin Duniya da ta hukunta majalisar dattawan Najeriya game da dakatarwar da aka yi mata.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *