Fadar shugaban Najeriya ta yi raddi ga Atiku kan yunwa

0
20250601_134212
Spread the love

Fadar shugaban Najeriya ta mayar da martani kan fargarwar da tsohon mataimakin shugaban ƙasar, Atiku Abubakar ya yi na cewa za a iya samu juyin-juya-hali, sakamakon matsananciyar yunwa da matsin rayuwa da ake fama da shi a ƙasar.

Fadar ta yi watsi da kalaman a matsayin tsohon tunani da aka riga aka wuce.

Inda ta bayana kalaman tsohon mataimakin shugaban ƙasar a matsayin na siyasa ne tsagwaran sa.

Gwamnatin ta kuma jaddada cewa matakan da gwamantin ke ɗauka tuni suka fara ɗora ƙasar kan hanyar farfaɗowar tattalin arziki a ƙasar.

Alhaji Atiku Abubakar ya zargi gwamantin Bola Ahmed Tinubu da samar da manufofi da ke ƙara ta’azzara hauhawar farashi, da rashin aikin yi, da ƙarancin abinci a ƙasar.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *