Fadar shugaban Najeriya ta yi raddi ga Atiku kan yunwa

Fadar shugaban Najeriya ta mayar da martani kan fargarwar da tsohon mataimakin shugaban ƙasar, Atiku Abubakar ya yi na cewa za a iya samu juyin-juya-hali, sakamakon matsananciyar yunwa da matsin rayuwa da ake fama da shi a ƙasar.
Fadar ta yi watsi da kalaman a matsayin tsohon tunani da aka riga aka wuce.
Inda ta bayana kalaman tsohon mataimakin shugaban ƙasar a matsayin na siyasa ne tsagwaran sa.
Gwamnatin ta kuma jaddada cewa matakan da gwamantin ke ɗauka tuni suka fara ɗora ƙasar kan hanyar farfaɗowar tattalin arziki a ƙasar.
Alhaji Atiku Abubakar ya zargi gwamantin Bola Ahmed Tinubu da samar da manufofi da ke ƙara ta’azzara hauhawar farashi, da rashin aikin yi, da ƙarancin abinci a ƙasar.
