Tinubu zai farauto tare da kawo karshen ku – NSA Ribadu ya yiwa ‘yan ta’adda barazana.

0
1000096843
Spread the love

Mai baiwa shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, NSA, Nuhu Ribadu, ya bayyana cewa gwamnatin shugaba Bola Tinubu za ta gano tare da farauto ‘yan ta’adda a duk inda suke.

Da yake magana a Abuja, NSA, ya ce gwamnatin Tinubu ta kuduri aniyar ganin an sa ‘yan ta’adda su fuskanci shari’a.

Hukumar ta NSA ta bada tabbacin cewa dukkan al’ummomi a fadin Najeriya za su kasance cikin koshin lafiya tare da kawar da ‘yan ta’adda a karkashin gwamnatin Tinubu.

Tun bayan hawansa karagar mulki, gwamnatin Bola Tinubu ta ci gaba da yaki da ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga a yankin arewacin Najeriya.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *