Wasu dattawan Katsina sun buƙaci gwamnati ta sauya salon yaƙi da ƴanbindiga a jihar

0
1000090584
Spread the love

Wasu dattawan jihar Katsina da ke yankin arewa maso yammacin Najeriya ƙarƙashin ƙungiyar kula da sha’anin tsaron ta Katsina wato Katsina Security Community Initiative ta yi kira ga duka gwamnatocin jihar da tarayya su ɗauki wani sabon salo wajen tunkarar matsalar ‘yan fashi daji a jihar.

Ƙungiyar ta yi wannan kiran ne a wajen wani taron da ta yi a Abuja a jiya Lahadi inda ta ce ci gaba da ƙaruwar matsalolin kashe-kashe da sace-sacen jama’a a jihar na nuna cewa matakan da ake ɗauka yanzu ba su aiki.

Dr. Bashir Kurfi shi ne shugaban ƙungiyar, inda ya bayyana wa BBC Hausa cewa ƴanbindiga suna da ƙarfi a wasu ƙananan hukumomin jihar, wanda hakan ya sa suke so a sabunta salo, tare da nemo wasu sababbin hanyoyin na yaƙi da matsalar tsaro.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *