Zan koma bakin aiki ranar talata duk abinda zai faru – Natasha.

Spread the love

Hoto – @natashaakpoti.

Sanata mai wakiltan Kogi ta tsakiya, Natasha Akpoti-Uduaghan, ta sha alwashin ci gaba da aikinta a majalisar dattawa a ranar Talata.

Akpoti-Uduaghan ta ce matakin da zata dauka ya yi daidai da hukuncin da kotu ta yanke.

Ta bayyana hakan ne a wata zantawa da ta yi da ‘yan jarida yayin da ta je mazabarta domin wani shirin horaswa a ranar Asabar.


‘Yar majalisar da ta shiga rudani ta ce dakatarwar ta takaita mata gudanar da ayyukanta na majalisar.

Natasha ta bayyana cewa a hukumance ta sanar da majalisar dattawa a rubuce game da aniyar ta na komawa.